Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Pages

Labarai:

latest

Ya Kamata A Goyi Bayan Shaikh Nura Khalid Saboda Gaskiyar Da Ya Fada -Shaikh Yaqoub Katsina

  Wakilin ‘yan’uwa Musulmi Almajiran Shaikh Ibraheem Zakzaky na Katsina, Shaikh Yakubu Yahaya Katsina ya bayyana goyonsa ga kalaman Shaikh...

 



Wakilin ‘yan’uwa Musulmi Almajiran Shaikh Ibraheem Zakzaky na Katsina, Shaikh Yakubu Yahaya Katsina ya bayyana goyonsa ga kalaman Shaikh Nura Khalid bisa abubuwan da yake faruwa na tabarbarewar tsaro a Nijeriya. Shehin Malamin ya bayyana hakan ne a jiya Lahadi a Markazinsu a yayin gabatar da Tafsirin Alkur’ani mai Girma na watan Ramadan.

Shehin Malamin ya ce; “Akwai wani Malami da na ji ya yi magana mai kama da irin wannan ko shekaran jiya Juma’a ne? Wani ko Nura Khalid ne? Ya yi magana a Masallacin Juma’a waj3n Pre-khudbarsa ya ce; a ki yin zabe sai an samu zaman lafiya. Abin da ya fada daidai ne kuma ya kamata Malamai su goyi bayansa ne amma munafukan duk sun yi shiru, karshe an ma tube shi (daga Limanci) ka ga ashe Malamai na tasiri, kun ga dama na ce maku matsalar tana wajen Malamai”, inji shi.

Ya ci gaba da cewa; “To duk munafukan sun yi shiru yanzu ma abin da suke gani laifinsa ne shi ya tsokano wa kansa wanda ya kamata a goyi bayansa ne kowa ya yi magana ya zama haka take sai ka ga sun sassauko. Aki yin zaben mana sai mene?” ya tambaya.

Ya kara da cewa; “Saboda haka Malamai su ji tsoron Allah su gayawa mutane gaskiya wannan Nura Khalid din gaskiya ya fadi kuma ya kamata a goyi bayansa ko da baka da ra’ayi irin nasa, ko baka cikin kungiyarsa amma abin da ya fada mafita ce ga al’umma cewa ka da a yi zabe in ba a yi zabe ba wani abu ne zai faru wanda zai ba mutane dama su samu sauki”.

No comments