Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Pages

Labarai:

latest

'Yan bindiga Sun Farmaki Fulani Sun Sace Mutum 10 Da Shanu 300 A Anambra

'Yan bindiga sun sace wasu Fulani makiyaya ‘yan kungiyar Miyatti Allah guda 10 a jihar Anambra tare da shanunsu 300. Rahotan...


'Yan bindiga sun sace wasu Fulani makiyaya ‘yan kungiyar Miyatti Allah guda 10 a jihar Anambra tare da shanunsu 300.

Rahotanni sun ce ‘yan bindigar sun bukaci a biya su Naira miliyan 4, a kuma hada musu da bindiga daga iyalan wadanda suka yi garkuwa da su.

Shugaban kungiyar ta Miyetti A na yankin Kudu maso Gabas, Alhaji Gidado Siddiki ya tabbatar da faruwar lamarin.

Siddiki, ya ce lamarin ya faru ne a Unguwar Obene da ke karamar hukumar Ogbaru a Unguwar makiyayan a lokacin da suke barci, da misalin karfe 1:30 na daren wayewar garin yau Asabar.

No comments