Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Pages

Labarai:

latest

YANZU-YANZU: Ofishin Shaikh Zakzaky Ya Fitar Da Labarin Ganin Jaririn Watan Ramadan A Nijeriya

Ofishin Jagoran Harkar Musulunci a Nijeriya, Shaikh Ibraheem Zakzaky ya fitar da sanarwar ganin jaririn watan Ramadan a fadin Ni...

Ofishin Jagoran Harkar Musulunci a Nijeriya, Shaikh Ibraheem Zakzaky ya fitar da sanarwar ganin jaririn watan Ramadan a fadin Nijeriya. 

Ofishin ya wallafa hakan ne a shafinsa na Facebook kamar yadda wakilin Jaridar MADOGARA ya labarto. 

Ofishin ya ce; "Mun sami rahotannin ganin jaririn watan Ramadanan na bana 1443". 

Ya ci gaba da cewa; "Garuruwan da aka gani yau Juma'ah sun hada da: 1.Birnin Kebbi. Al'ummar gari da yawa sun gani a Unguwar Illelar Yari. 2. Jimeta, Jihar Adamawa. 3. Ringim, Jihar Jigawa. 4. Unguwar Inwala, Damagaram, Jumhuriyar Nijar", ya labarto. 

Ya kara da cewa; "Har yanzu ana samun karin rahotanni. Don haka gobe Asabat zai zama 1 ga Ramadan 1443, in sha Allah", suka jaddada. 

No comments