Mai Alfarma Sarkin Musulmin Nijeriya Muhammad Saad Abubakar ya yi Allah wadai da kisan da aka yi wa wata dalibar Babbar Kwalejin Ilimin Ji...
Mai
Alfarma Sarkin Musulmin Nijeriya Muhammad Saad Abubakar ya yi Allah wadai da
kisan da aka yi wa wata dalibar Babbar Kwalejin Ilimin Jihar Sokoto da aka
zarga da batanci ga Manzon Allah tsira da Amincin Allah suka tabbatar a gare
shi.
Wata
sanarwar da fadar Sarkin ta gabatar mai dauke da sanya hannun Sakataren
Masarautar kuma Danburan din Sokoto, Saidu Muhammadu Maccido ta yi Allah wadai
da kisan inda ta bukaci jami’an tsaro da su tabbatar da gurfanar da wadanda suka
aikata laifin a gaban shari’a.
Masarautar
ta bukaci jama’ar Sokoto da kasa baki daya da su ci gaba da zaman lafiya a
tsakanin su, yayin da jami’an tsaro ke gudanar da aikin su.
Tuni
gwamnatin Jihar Sokoto ta sanar da rufe Kwalejin da kuma kaddamar da bincike
akan lamarin kamar yadda kwamishinan yada labarai Isa Bajini Galadanci ya
tabbatarwa RFI Hausa.
Rahotanni
sun ce wasu fusatattun dalibai ne suka yiwa dalibar Kwalejin da ake kira
Deborah duka da kuma cinna mata wuta saboda zargin da suka mata na cin zarafin
addinin Islama.
Wani
daga cikin daliban Kwalejin ya ce Deborah ta yi kalamun batancin ne a wata
kafar sada zumunta da suke amfani da ita, abin da ya haifar da tashin hankalin.
Yanzu
haka ana ci gaba da tafka muhawara a kafofin sada zumunta dangane da kisan,
inda jama'a ke bayyana ra'ayoyi mabambanta dangane da kisan.
Rundunar
‘Yan Sandan Jihar Sokoto ta sanar da kama mutane 2 da ake zargin suna da hannu
wajen aikata kisan.
No comments