Dan takarar gwamna a karkashin inuwar Jam'iyyar PDP a Kaduna, Isa Ashiru Kudan ya bayyana cewa al'ummar jihar na cikin k...
Dan takarar gwamna a karkashin inuwar Jam'iyyar PDP a Kaduna, Isa Ashiru Kudan ya bayyana cewa al'ummar jihar na cikin kunci a karkashin mulkin Gwamna Nasiru El-Rufai.
Inda Isa Ashiru Kudan ya yi kira ga gwamnan da ya janye korar ma'aikata da yake yi ba ji ba gani; "ina kira ga Mallam Nasiru Ahmad El-Rufai da ya dakatar da koran ma'aikata da yake ci gaba da yi, al'umma jihar Kaduna a halin yanzu suna fuskantar matsaloli rayuwa daban-daban, idan ba a tallafa musu ba to bai kamata a ce ana raba su da ayyukan da suka dogara da shi don ciyar da iyalansu ba, korar ma'aikata a wannan yanayi na tsadar rayuwa shi ne mafi munin nau'in zalunci", inji shi.
Idan za a iya tunawa Gwamnatin jihar Kaduna ta sanar da korar malamai 2,356, da suka gaza cin jarrabawar gwaji da aka yi musu ciki harda shugaban Kungiyar Malamai ta Nijeriya reshen jihar.
No comments