Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

An Kama Wanda Ake Tuhuma Da Laifin Hada Bama-Bamai A Taraba

  'Yan sanda a Jihar Taraba da ke Najeriya sun kama wani mutumin da suke tuhuma da laifin hada bama-bamai. An kama mutumin ne a garin Te...

 


'Yan sanda a Jihar Taraba da ke Najeriya sun kama wani mutumin da suke tuhuma da laifin hada bama-bamai.

An kama mutumin ne a garin Tella da ke karamar hukumar Gassol ta jihar a ranar Laraba.

Jaridar Daily Trust ta wallafa cewa an gano wasu kayayyakin hada bam a gidan mutumin, wanda ya mayar masana'anta.

An kuma gano wasu bindigogi da harsasai a gidan.

Jami'an 'yan sanda sun ce mutumin dan asalin Jihar Zamfara ne, kuma ana tsare da shi a shalkwatar 'yan sandan da ke Jalingo.

An kai wani jerin hare-hare da bama-bamai a watan jiya a cikin Jihar ta Taraba.

Kakakkin rundunar 'yan sanda a jihar, DSP Usman Abdullahi ya tabbatar wa jaridar Daily Trust aukuwar lamarin da kama wanda ake tuhumar.

No comments