Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

Ƙarin Bayani Kan Rasuwar Sarkin Kotorkoshi Bayan Shekara 61 A Kan Mulki

  Mun samu ƙarin bayani game da rasuwar Sarkin Kotorkoshi Mai Martaba Ahmad Umar da ke Jihar Zamfara, wanda ya mutu a yau Alhamis. Sarkin ya...

 


Mun samu ƙarin bayani game da rasuwar Sarkin Kotorkoshi Mai Martaba Ahmad Umar da ke Jihar Zamfara, wanda ya mutu a yau Alhamis.

Sarkin ya rasu yana da shekara 89 da haihuwa.

Ya hau kan karaga a ranar 17 ga watan Maris na shekarar 1961.

Bayanai sun nuna cewa sarkin ya rasu a gidansa bayan ya sha fama da jinya.

Wata sanarwa da gwamnatin jihar ta fitar ta ce za a yi jana'izarsa a yau da ƙarfe 6:30 agogon Najeriya a fadarsa da ke Kotorkoshi ta Ƙaramar Hukumar Bungudu.

A watan Maris na 2021 ne aka yi bikin cikar mai martabar shekara 60 a kan karagar mulki.


-BBC Hausa

No comments