Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Pages

Labarai:

latest

Jami'ar MAAUN Ta Nada Dr Abubakar Uwais A Matsayin Mataimakin Shugaba Bangaren Gudanarwa Kuma Magatakarda

Shugaban Majalisar Gudanarwar Jami’ar Maryam Abacha American University (MAAUN), Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo, a madadin Majali...



Shugaban Majalisar Gudanarwar Jami’ar Maryam Abacha American University (MAAUN), Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo, a madadin Majalisar, ya amince da nadin Dakta Habib Abubakar Awais a matsayin mataimakin shugaba bangaren gudanarwa/Magatakarda na MAAUN Kano a Nijeriya.

Farfesa Abubakar Gwarzo ne ya sanar da nadin a wata sanarwa da ya rabawa manema labarai a Kano a ranar Juma’a.

A cewar sanarwar, Abubakar Awais Babban Malami ne a Sashen Turanci da Harsunan Turai a Kwalejin Ilimi da Nazarin Ilimi a matakin Farko ta Jihar Kano (KASCEPS).

Har ila yau, Ma'aikaci ne a Jami'ar Maryam Abacha American University ta Nijer kuma Daraktan Ayyuka na Cibiyar Raya Ƙasashen Duniya (ICDI). 

"Dr Abubakar Uwais har wala yau Babban Jami'i ne a Kamfanin 'Classic Consulting Firm' kuma ya kasance mai ba da shawara mai zaman kansa a Ofishin Jakadancin Amurka a Abidjan, dake kasar Cote d'Ivoire sannan kuma mai bincike ne kan adabin turanci a Jami'ar Sultan Zainal Abidin (UniSZA) dake Malesiya," Sanarwar ta jaddada. 

No comments