Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

MAAUN Nijar Ta Jajantawa Iyaye Bisa Rasuwar Dalibarta, Salamatou Salissou Issa

  Hukumar gudanarwar Jami’ar Maryam Abacha American University ta Jamhuriyyar kasar Nijer (MAAUN) da ke Maradi, ta jajantawa iyayen wata dal...

 


Hukumar gudanarwar Jami’ar Maryam Abacha American University ta Jamhuriyyar kasar Nijer (MAAUN) da ke Maradi, ta jajantawa iyayen wata dalibar Jami’ar, Salamatou Salissou Issa, wadda ta rasu a ranar Asabar, 11 ga watan Yunin 2022 a Maradi dake jamhuriyar Nijar bayan takaitacciyar rashin lafiya.

 

Kafin rasuwarta, marigayiyar daliba ce ta digiri a matakin aji (200) a Jami'ar inda take karantar darasin huldar kasa da kasa.

 

Sakon ta’aziyyar na kunshe ne a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun shugaban Jami’ar MAAUN Nijar, Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo, wacce aka rabawa manema labarai kwafin a Kano a ranar Lahadi.

Hukumar gudanarwa ta MAAUN ta bayyana rasuwar dalibar a matsayin babban rashi ba kawai ga iyayenta da ‘yan uwanta kadai ba har ma da daukacin ma’aikata da daliban jami’ar.

 

Shugaban na MAAUN ya kuma bayyana Marigayiyar a matsayin daliba mai tarbiyya mai mutunta dattijai da sauran mutane musamman malamanta.

 

“A don haka, a madadin Hukumar Gudanarwar Jami’ar Maryam Abacha American University ta Nijar, ina son mika ta’aziyyarmu ga iyaye da ‘yan’uwa da abokanan marigayiyar.

"Mahukuntan Jami'ar suna kuma jajantawa gwamnatin Jamhuriyar Nijar da daliban jami'ar bisa rasuwar Salamatu Salissou Issa, Allah ya gafarta mata kurakuranta," in ji Farfesa Abubakar Gwarzo.

 

Ya roki Allah Madaukakin Sarki da ya jikan marigayiyar ya kuma sanya ta a Aljannar Firdaus, ya kuma bai wa iyayenta hakurin jure wannan rashi mara misaltuwa.

 

Issa, wacce ta rasu tana da shekaru 19 a duniya, tuni aka binne ta a garinsu na Maradi na Jamhuriyar Nijar kamar yadda addinin Musulunci ya tanada.




No comments