Kungiyar kwallon kafa ta Arsenal ta faro gasar Europa da kafar dama, bayan da ta doke FC Zurich har gidanta da kwallaye 2 da 1. Arsenal ne...
Kungiyar kwallon kafa ta Arsenal ta faro gasar Europa da kafar dama, bayan da ta doke FC Zurich har gidanta da kwallaye 2 da 1.
Arsenal ne suka fara cin kwallo a wasan ta hannun dan wasan da ya ke yi mata wasa a karon farko, Marquinho wanda ya saka kwallon da Eddie Nketiah ya gara masa.
Sai dai kafin hutun rabin lokaci 'yan wasan Zurich suka farke wannan kwallo daga bugun daga kai- sai- mai tsaron- raga, wanda Mirlind Kryeziu ya buga, bayan rafke Ola Selnaes da Nketiah ya yi.
Ana dawowa hutun rabin lokaci ne kuma, Nketiah ya ci wata kwallo da ta sanya Arsenal a gaba da taimakon sabon dan wasansu, Marquinho.
Yaran na Mikel Arteta za su fafata da PSV Eindhoven a wasansu na 2 a matakin rukuni a gasar cin kofin na Europa a Alhaamis mai zuwa.
No comments