Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Pages

Labarai:

latest

Ƙungiyar kare haƙƙin mata da yara sun gabatar da zanga-zanga a Zariya

A ranar alhamis ɗin data gabata ne 13/October/2022 ƙungiyar kare haƙƙin mata da yara tare da haɗin gwiwar lauyoyi da ke garin Za...



A ranar alhamis ɗin data gabata ne 13/October/2022 ƙungiyar kare haƙƙin mata da yara tare da haɗin gwiwar lauyoyi da ke garin Zariya da kewaye suka fito zanga-zanga akan karen haƙƙin mata da yara. Zanga-zangar na nuni ne da a daina matsa wa mata akan auren dole tare da tofin ala tsine akan masu fiyaɗe. 

Wannan zanga-zangar ta samu rakiyar jami’an tsaro mabanbanta. Mun yi ƙoƙarin jin ta bakin ɗaya daga cikin masu zanga-zangar amma haƙar mu bata cimma ruwa ba. Sai dai abin da muka lura masu zanga-zangar suna lurantarwa shi ne a daina matsa wa ƴaƴa mata akan auren dole. Sannan kuma abin kunya ya ƙare ga namiji mai yiwa mata fiyaɗe.


-Daga Mustapha Muhammad wakilin Jaridar Mafita da ke Birnin Zazzau da kewaye.

No comments