Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Pages

Labarai:

latest

Hukumar NUC Ta Ziyarci Sabuwar Jami’ar Franco-British International Da Ake Son Kafawa A Kaduna

  Wata tawaga daga hukumar lura da jami’o’in kasa wato NUC ta kai ziyarar tantancewa a jami’ar Franco-British International University dake ...


 

Wata tawaga daga hukumar lura da jami’o’in kasa wato NUC ta kai ziyarar tantancewa a jami’ar Franco-British International University dake Kaduna.

Tawagar wacce ke karkashin jagorancin Mataimakin Darakta, a bangaren lura da Babban shiri da samar da kayayyakin da ake so, Dr. Mustapha Rasheed, ta isa Kaduna ne a ranar Asabar 28 ga watan Janairu, 2023, domin tantance kayan aikin da aka tanada a jami’ar da ake yunkurin samarwa.

Kayayyakin da tawagar ta ziyarta sun hada da dakunan karatu da manyan dakunan taruka, dakunan gwaje-gwaje, dakunan ajiye littafai, ofisoshin ma’aikata da kuma dakunan kwanan dalibai da wuraren ma’aikata.

Tawagar ta samu tarba ne bayan ta isa wurin daga wanda yake son samar da Jami’ar, Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo tare da kwamitin tsare-tsare da aiwatarwa wanda suka dukufa wajen ganin jami’ar da ake son a kafa ta samu shawarwari daga NUC domin ganin an ba ta lasisin soma aiki a matsayin jami’a mai zaman kanta a Nijeriya cikin kankanin lokaci.

A ziyarar da tawagar ta kai Jami’ar FBI da ke Cibi Close ta hanyar Nnamdi Azikiwe Expressway a Kaduna, ta zagaya lungu da sako na Jami’ar baya ga ziyartar wasu muhimman wurare a wannan jami’ar.

Bayan tantance kayayyakin aikin, tawagar ta NUC da membobin kwamitin Tsare-tsare da aiwatar da Jami’ar a karkashin jagorancin Dakta Abdullahi Abubakar Kankia sun yi zama inda aka tattauna kan manyan sakamakon binciken da kuma bayar da shawarwari masu ma’ana.

Sauran jami’an hukumar ta NUC sun hada da Engr. Sulaiman Adebayo, Mataimakin Darakta a ofishin Darakta, Malam Abubakar Nuhu, mataimakin Darakta kan harkokin ilimi, Barista Ummukultum Giwa, Mataimakiyar Darakta kan sha’anin mulki da shari’a, da Lola Agawo, ma’aikacin Sakatare.

Jami’ar Franco-British International, Kaduna na daya daga cikin Jami’o’i hudu da Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo ya kafa.

 

 

No comments