Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

Tinubu Ya Yi Ta’aziyyar Rashin Dattijon Kasa, Musa Musawa

  Zababben shugaban kasa Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ya bayyana alhininsa kan rashin dattijon kasa, Alhaji Musa Musawa. An haife shi ne a rana...

 


Zababben shugaban kasa Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ya bayyana alhininsa kan rashin dattijon kasa, Alhaji Musa Musawa.

An haife shi ne a ranar 1 ga Afrilu, 1937, marigayin ya kasance mai yada labarai, jami'in diflomasiyya kuma hazikin dan siyasa. Ya rasu ne a ranar Talata bayan ya sha fama da rashin lafiya.

Alhaji Musa Musawa ya rasu ya bar ‘ya’ya da dama da sauran ‘yan’uwa da suka hada da mataimakiyar mai magana da yawun kungiyar yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar APC, Barista Hannatu Musawa.

A cikin wata sanarwa da aka fitar da yammacin ranar Talata daga ofishin yada labaransa, wanda Abdulaziz Abdulaziz ya sanyawa hannu, Asiwaju Tinubu ya bayyana marigayin dan jihar Katsina a matsayin daya daga cikin ‘yan gwagwarmayar neman ‘yancin kai na Nijeriya.

“Hakika shi mutum ne mai zurfin tunani da son ci gaba. Tun yana matashi ya hada karfi da karfe tare da takwarorinsa masu ra’ayi daya a rusasshiyar kungiyar ‘Northern Elements Progressive Union (NEPU)’ wajen fafutukar kwato ‘yancin kai tare da kwato ‘yancin jama’armu baki daya.

“A shekarun baya bayan samun ‘yancin kai, Alhaji Musa Musawa ya ci gaba da hada kai da kungiyoyi dake son kawo ci gaba a ciki da wajen siyasa domin ciyar da talakawa da wadanda ake zalunta gaba a cikin al’umma.

“Ya kasance dan siyasa mai son ci gaba wanda ya sauke nauyinsa a matsayinsa na mai kishin kasa. Nijeriya ta yi rashin hazikin danta kuma za mu yi kewar shawararsa ta uba a lokacin da muka fi bukata,” in ji Tinubu.

Zababben shugaban kasar ya roki Allah madaukakin Sarki da ya gafartawa Dattijon da ya rasu kurakuransa, ya kuma bai wa iyalansa hakurin da ake da bukata a lokacin bakin ciki.


No comments