Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Pages

Labarai:

latest

Shekaru Sama Da 200 Da Kafa Gidan Kanawan Likoro: Sun Yi Taron Karfafa Zumuncin Dake Tsakaninsu

Wasu daga cikin mahalarta taron Gidan Kanawan Likoro Daga Ammar M. Rajab Kamar yadda suka saba a duk shekara, Gidauniyyar Gidan Kanawan Li...

Wasu daga cikin mahalarta taron Gidan Kanawan Likoro

Daga Ammar M. Rajab

Kamar yadda suka saba a duk shekara, Gidauniyyar Gidan Kanawan Likoro na shirya taro domin sada zumuncin dake tsakaninsu. A bana ma gidauniyyar ba ta yi kasa a guiwa ba, sun shirya irin wannan taro a ranar Litinin 24 ga watan Afrilun 2023 daidai da 4 ga Shawwal, 1444.

Gidan Kanawan Likoro an kafa shi ne shekaru fiye da 200 a garin Likoro dake karamar hukumar Kudan ta jihar Kaduna ta yau. Malam Ibrahim, wani Dattijo mai shekaru 64 a duniya ya tabbatar da cewa; gidan ya samo asali ne a shekarar 1812 a lokacin da ake karbar baki daga ko’ina da suka sauka a garin na Likoro; “bayan kamar shekaru kamar 50 zuwa 60 da kafa gidan Kanawan Likoro aka yi zauren gidan Kanawa wanda yanzu yake da shekaru 150”, a cewar Malam Ibrahim a yayin da yake gabatar da tarihin gidan a lokacin taron.  

Malam Ibrahim ya ci gaba da cewa; “duk wanda ka ganshi a taron nan na yau ka dauke shi a matsayin dan uwanka ne”. Ya kuma kara da cewa; a yanzu suna da mutane daban-daban da suka fito daga gidan wanda ya ce; suna da Malamai, ‘yan kasuwa, manoma da ma’aikatan gwamnati a matakai daban-daban. Ya nusasshe da cewa; gidan ya zama sananne tun daga Legas har Maiduguri; “an san babban zauren gidan Kanawa”, inji shi.

Malam Ibrahim, Dattijo mai shekaru 64.

Ya kuma labarta cewa; gidan na da sassa daban-daban wanda suka zama zuri’ar gidan wanda ya hada da sassan Alhaji Garba, Malam Yakubu Likoro, Nagoroji, Malam Sule da sauran su.

Sheikh Jamilu Saleh daya ne daga cikin zuri’ar gidan, a na shi jawabin ya karfafa ne akan muhimmancin sada zumunci. Inda ya kawo ayar Allah dake nuni da cewa; yankewa da kin sada zumunci barna ne a bayan kasa. Sannan ya kawo hadisin Manzon Allah (S) da yake cewa; duk mai son tsawon rai a duniya, to ya sada zumunci. “zumunci abu ne mai fadin gaske da girma”, ya kara nanatawa. Sannan ya karkare da karfafa su da yin hakuri da juna.

Sheikh Jamilu Saleh

Shugaban Gidauniyyar ta gidan Kanawan Likoro na kasa, Dan Asabe Ibrahim, a na shi bayanin ya bayyana cewa gidauniyyarsu ba ta siyasa ce ba ta kuma nuna bangarancin addini ko fahimta bane. Sannan ya lurantar da cewa; gidauniyyar ta su ta karfafa asali da zumunta ne.

Sannan ya yi tilawar ayyukansu wanda ya ce ya hada da ziyarorin sada zumunci, ziyarar asibitoti, daurin aure, ta’aziyyah, hada aure, sasanci, ayyukan jin kai da sauran su. Shugaban ya ce; “tarihin Likoro ba zai cika ba sai an fado gidan Kanawan Likoro”, inji shi.

Sai dai ya ce daga cikin aikin da suka yi harda gyaran zauren gidan Kanawan Likoro wanda ya shafe shekaru fiye da 150; “ba za mu zura ido zauren ya lalace a zamaninmu ba shiyasa muka gyara shi”, ya tabbatar.

Shugaban ya ce a nan gaba suna fatan a taro irin wannan su rika hada wa da daurin auren zumunci a tsakanin ‘ya’yan gidauniyyar. “aure na daga cikin abin da ke hada zumunci”, ya nusasshe.

Dan Asabe Ibrahim, shugaban Gidauniyyar Gidan Kanawan Likoro yana gabatar a yayin taron.

Ya nemi da dukkanin ‘ya’yan gidauniyyar da su ci gaba da bai wa gidauniyyar gudummawa domin ci gaban ayyukansu; “ilimi, kasuwanci, tarbiyyah, al’amuran da suka shafi jama’a, samar da cibiyoyi na lafiya da na dogaro da kai na daga cikin kudurorin kungiyarmu”, ya tabbatar.

A yayin ganawarsa da manema labarai, ya yi karin haske da cewa; “mun samu nasarori sosai, babban nasarar da muka samu akalla a zumuncin nan mun aurar da mata da maza akalla guda biyar. A irin wannan taron wani ya ga wata, wata ta ga wani, mun aurar, na daya ke nan. Na biyu; akwai wadanda aurensu ke tangarda mun yi nasarar yanzu suna zaman lafiya. Akwai yaran da muka samo musu aikin yi. Akwai wadanda muka samo musu gurbin karatu. Akwai wadanda ba su da lafiya mun dauki nauyin rashin lafiyarsu”, ya tabbatar.

“burinmu shi ne mu ga wannan abin da na lissafa maka ya ci gaba. Misali; yaran nan da muka samo musu gurbin karatu idan sun kammala mu samo musu aikin yi. Akwai wadanda su kuma ba karatu bane a gabansu sana’o’i ne, mu ga cewa mun samo musu sana’ar yi”, ya lurantar.

Dan Asabe Ibrahim, ya bayyanawa wakilinmu cewa sun gaji kungiyar ne daga wajen iyayensu shekaru 10 da suka gabata. Kuma suna da shugabannin a kasashen Saudiyya da Nijer, da ma dukkanin kananan hukumomin Nijeriya.

Kungiyar a yayin taron ta karrama Alhaji Bello Abubakar Annur, shugaban kungiyar manoma ta Nijeriya kuma daya daga ‘ya’yan kungiyar bisa Sarautar Danburam na Funtuwa da ya samu.

A yayin karramawar.

Daga nan ne aka bai wa wakilan yankuna da suka hada da Fulatan, Zarewa, Funtuwa, Zariya, Kaduna, Guibi, da kuma Kano damar bayar da shawarwari ga kungiyar.

A yayin zantawarmu da Alhaji Sani Yushau, Mai Anguwan Anguwar Kanawan Likoro ya ce abin da yasa suke karfafa batun auren zumunci a tsakaninsu shi ne “don kada zumunci ya yi mana nisa, shiyasa muke karfafa wannan maganar aure”.

Alhaji Sunusi, Sarkin Guibi, wanda ya fito daga garin Guibi ta karamar hukumar Kudan ya ce, ya yi matukar jindadin halartar taron, inda ya yi kira ga dukkanin wadanda suke gidan Kanawa, su so junansu da gaskiya; “ya zama abin ba a baki kawai yake ba. Mu taimaki ‘yan’uwanmu da gaske. Mu duba ‘yan’uwanmu wadanda ba su da abin yi a ba su abin yi domin wannan shi zai karfafa zumunci. Sannan sai auratayya ta wannan yanayin zumuncin zai kara karfafa”, ya tabbatar.

Ya kuma karfafa kiransa akan shugabannin kungiyar da cewa; “kiran da nake yi ga shugabannin kungiya da su tsaya su natsu su yi nazari, su gane cewa matasan nan dalibai ne ko kuma wadanda ba sa karatu; idan wadanda suke karatu ne wacce hanya za a taimake su, idan kuma wadanda suka gama ne wacce hanya za a bi a taimake su a kan abin da ya shafi kasuwanci ko aikin gwamnati.”
Alhaji Sunusi, Sarkin Guibi a yayin ganawa da 'yan jarida.

Shima Alhaji Isiyaku Sadiq, Sarkin Zangon Shanun Zazzau, ya ce ya ji dadin wannan taron domin taron ya sake karfafa zumuncinsa da wasu. Sannan taron na bana ya fi tarukan baya armashi da bunkasa.

Shugabar mata ta kungiyar, Malama Rukayyat Sa’id ta ce tana alfahari da kungiyar, kuma daga cikin nasarar da ta samu a matsayinta na shugabar mata ta kungiyar shi ne ta hada auratayya da kuma sasanta ma’aurata.

Ta yi kira ga mata matasa na kungiyar da su dora daga inda suka tsaya ko bayan ba su inda ta ce; “mu yanzu abin da muka yi tamkar dora gini ne, mun dora musu ginin arziki muna son su dora bulo mai nauyi wanda yake sun wayi gari sun ga muna yi, suma su dauki hannu su ci gaba. Wannan tafiya dari bisa dari mu dunga tafiyar da shi har ko bayan ba mu. Suma ‘ya’yansu su taso su ga abin da suke yi, jikokinsu su taso su ga abin da suke yi”, ta lurantar.

Malama Rukayyat Sa’id

Taron na bana ya gudana ne a Kwalejin gwamnati ta Commercial dake Hayin Ojo a karamar hukumar Sabon Gari ta jihar Kaduna. Wanda aka soma shi da misalin karfe 11 na safe bayan budewa da addu’a da kuma karatun Alkur’ani mai girma daga Mulaikat daga Kaduna sai kuma Aminu Sulaiman daga Kano. 





No comments