Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

Zaben Zamfara 2023: Gwamna Matawalle Da Tatsuniyar Amfani Da Karfin Soja

  Daga Sulaiman Bala Idris Fassarar Muhammad A. Abubakar A wata hira da sashen Hausa na DW, gwamnan jihar Zamfara mai barin gado, Bello Moha...

 

Daga Sulaiman Bala Idris

Fassarar Muhammad A. Abubakar

A wata hira da sashen Hausa na DW, gwamnan jihar Zamfara mai barin gado, Bello Mohammed Matawalle, ya yi wani ikirari kan dalilan da ya sa ya sha kaye a zaben da ya gabata. Sannan ya yi zargin cewa an yi amfani da karfin soja domin dakile damarsa.

Shan kayen da Matawalle ya yi shi ne babban kaduwa a babban zaben 2023. Ya sha kaye ne a hannun wani tsohon ma’aikacin banki da bangaren jam’iyyar APC ke yi masa ba’a a matsayin dan siyasar da bai da gogewar da ake da bukata domin lashe zaben karamar hukuma. Sai dai a wani yanayi na daban, a hukumance an bayyana wannan dan siyasar da ba shi da kwarewa a matsayin zababben gwamnan jihar.

Abin da ya faru a Zamfara wani gangamin taron dangi ne da wasu wanda suka hada da shugaba mai ci, da tsoffin gwamnoni uku, da duk wasu manyan ‘yan siyasa da suka hada kai suka fafata da wani sabon dan siyasa da ya shiga harkar siyasar a shekarar 2018. Hakika wannan sauyi ne na siyasar karni da aka rubuta shi da babbar tawada a tarihin siyasar jihar Zamfara.

Matawalle da jam’iyyar APC sun yi amfani da duk wata dama domin yin magudin zabe, tun daga kan kokarin kawo cikas ga zaben zuwa sace tattara sakamakon zabe daga rumfunan zabe, Unguwanni, da kuma kananan hukumomi.

Wannan dai shi ne Matawallen da ake zargin da ya sace jami’in hukumar zabe ta INEC na garinsu, wato karamar hukumar Maradun, domin sake rubuta sakamakon zabe tare da ware wa kansa kuri’u na bogi da ba za su misaltu ba—godiya ga shafin IREV dake tattara sakamakon zabe bisa wannan ceto.

Yana da matukar wahala a yarda cewa babban mai bayar da tsaro na jihar da ‘yan bindiga suka addaba ne zai fito a fili ya yi ikirarin cewa an girke sojoji 50 a kowace rumfar zabe a fadin jihar. Wannan magana ta isa dalilin da yasa mutanen Zamfara suka ki Matawalle. Ya yi nuni da cewa bai san tsarin tsaro na kasar nan ba, gami da jimillar ma’aikatan da ke aiki a kowanne sashen tsaro.

Jihar Zamfara na da jimillar rumfunan zabe 3,529. Ban san wanda ya koyar da gwamna ilimin lissafi ba, amma dole ne ya zama malami mai ban tsoro. Idan kun ninka 50 sau 3,529, zaku sami 176,450.

Misalin Gwamna Matawalle shi ne sojoji 176,450 aka tura Zamfara. Mu fada masa gaskiya ne ko kuma mu bar shi gaskiyar ta tashe shi daga barci? Mafi kyawun zaɓin da ya rage masa shi ne ya mutunta zabin mutane tare da yin ritaya cikin shiru domin ya ceci kansa daga ƙarin kunya.

Rundunar sojin Nijeriya na da sojoji kusan 230,000, amma Gwamna Matawalle na son ya nuna cewar sojoji 53,550 ne kawai aka tura su wasu jihohin Nijeriya a ranar zaben gwamna; sauran sojoji 176, 450 an tura su ne Zamfara.

 

A wannan lokaci, yana da wahala ga duk mai hankali ya fahimci me Matawalle ke Æ™oÆ™arin tabbatarwa da maganarsa domin ya saba wa hange da hankali. Ko da yake, ya saba dama, a lokuta da daban-daban, yana tabbatar da sakacinsa a ayyukansa har ma da kalamansa. Za mu iya kau da kai da wasu kalamai na gwamnan wanda ya yi amannar cewa sauya sheka zuwa jam’iyyar APC mai mulki ne kadai zai sabunta masa nasarar takararsa ta biyu. Dole ne har yanzu yana cikin tsananin kaduwa. Amma maganganun rashin hankali da ka iya karkatar da gaskiya sune abin da ba za a taÉ“a yarda da su ba.

Hukuncin ikirarin Gwamna Matawalle KARYA ce. Ba dalibin firamaren da zai fahimci wannan iƙirari na ban dariya. Gwamnan ya bayyana ne domin kawai ya samu masu tausaya masa. Yana kokarin ya sauya labarin cewa mutane ne suka yi watsi da shi kuma suka ki shi, suka kada shi.

Al’ummar Zamfara masu juriya sune wadanda suka toshe duk wata hanya domin yin magudi, sannan bai kasance kasuwanci ba kamar yadda aka saba. Tabbas matasan jihar Zamfara da suka gaji da salon mulkin Matawalle ne suka haddasa faduwarsa. ‘Yan fansho da aka cire musu kudadensu daga tsarin fansho wanda ba a san inda aka sa ba suna daga cikin wadanda suka kayar da shi.

Duk baya ga haka nan, abin da ya faru da Matawalle daga Allah ne. Kada ya manta, an dauke shi a wani faifan bidiyo yana cewa: “Idan har na taba cin amanar PDP, kada Allah yasa na zauna lafiya har zuwa karshen rayuwata, na rantse da Allah. Idan har zan iya barin PDP ko kuma na yaudari daya daga cikin membobinmu, Allah ya hukunta ni.”

Maganar ta isa haka nan, mai girma gwamna. Yanzu lokaci ne da za ka duba baya ka kuma tuba. Farin wata sabuwa ce ta bayyana ga jihar Zamfara.

Bala ya rubuto ne daga Gusau ta jihar Zamfara.

 

No comments