Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

Zamfara 2023: Ƙawancen Marasa Tsarki Da Nasarar Dauda Lawal Mara Aibi

  Daga Sulaiman Bala Idris “Kun yi failing, ku zo ku kwashe kayanku…” Kuskure na farko da jam’iyyar APC reshen jihar Zamfara ta yi shi ne, d...

 


Daga Sulaiman Bala Idris

“Kun yi failing, ku zo ku kwashe kayanku…”

Kuskure na farko da jam’iyyar APC reshen jihar Zamfara ta yi shi ne, daukar wakar da ke sama da wasa, wanda za a iya fassarata da cewa ‘Kun fadi, ku zo ku kwashe kayanku’. Ga shi nan dai! A ranar 29 ga Mayu, jihar Zamfara za ta shaidi wani sabon fuska da sabon farawa – gwamnatin Dauda Lawal.

Daga cikin abubuwa masu girgizarwa a zabukan 2023 a Nijeriya akwai guguwar tsunami ta siyasa da ta kawo karshen mamayar sama da shekaru goma na gaggan ‘yan siyasa a siyasar jihar Zamfara. Dukkanin manya-manya wadanda ake kambama kimar siyasarsu sun hada karfi da karfe a sansani guda a karkashin inuwar jam'iyyar APC, a karon farko tun bayan komawar mulkin dimokuradiyya da jam'iyyar PDP ta karya lagon cin zabe a jihar Zamfara.

Tsoron zama a jam'iyyar adawa ta PDP ne ya sa Gwamna mai barin gado, Bello Matawalle ya yanke shawarar sauya sheka daga jam'iyyar zuwa APC mai mulki, cike da fatan gwamnatin Tarayya za ta kubutar da shi, bugu da kari, a kuma dakatar da duk wani dan siyasa daga jam'iyyar yin takara.

Hasashen Matawalle kamar na mayaki shi kaɗai ne a cikin yaƙi da ƙwararru da gogaggun mayaka. Wani mataki ne na tsoro da zakuwa domin kaucewa murkushewar hadakar mutum biyu na Abdulaziz Yari da Kabiru Marafa ya sanya shi daukar matakin yarinta na sauya sheka - komawar da ta kusan tsaga jam'iyya mai mulki a jihar, amma zakuwa, son kai, da kuma yunwar mulki ta sa aka yi nasarar wannan auren na daidaito da gwamna mai barin gado da kuma wadanda ake kira jaruman jam’iyya.

Manazarcin siyasa zai gaya maka cewa kawancen da aka yi a Zamfara na APC tunda fari an yi shi bisa rashin fahimta saboda kwadayi da hassada da neman mulki. Burin Matawalle shi ne tabbatar da takararsa ta biyu; Burin Abdulaziz Yari shi ne ya tabbatar da samun nasarar kujerarsa ta Sanata; Haka ma ga Sanata Kabiru Garba Marafa, yaki ne na neman kujerar Sanatan tsakiya.

Dukkanin wannan lissafe-lissafe na siyasa da kuma murda-murdar siyasa an tsara su ba tare wani daga cikin masu wannan tsare-tsaren sun yi la’akari ko kuma ganin Dauda Lawal a matsayin barazana ba. Suna ɗaukarsa a matsayin dan koyo wanda da ƙyar ya kwaci kansa daga dambatawa da su.

A yayin da rikicin jam’iyyar APC ya lafa, Gwamna Matawalle ya shiga jam’iyya mai mulki, aka yi sulhu da ‘karfi’ da Abdulaziz Yari da Marafa; Sai da gwamnatin tarayya da duk masu ruwa da tsaki a jam’iyyar APC suka shiga tsakani domin hadakar ta tabbata. Babu wani daga cikin masu ruwa da tsaki na jam’iyyar a matakin kasa da jiha da yake da hangen nesan daukar Dauda Lawal a matsayin barazana. Zamfara ta samu, haka suka yi imani.

Bisa ga wannan yanayi, tsohon babban ma’aikacin bankin ya yanke shawarar sauya sheka zuwa jam’iyyar PDP, wanda wannan ya kasance mafarin sabon yanayi a tarihin siyasar jihar. Gwamnan, jam’iyyar APC a matakin jiha da kasa, suka yi raha game da sauya shekar. Yari da Marafa suka yi takamar cewa sune ‘masu’ siyasar Zamfara.

Gwamna mai barin gado ne ya gane kololuwar dacewar siyasar Dauda a daidai lokacin da ‘bakin alkalami ya riga ya bushe’. Yanayin siyasar jihar ya kara zafi ne bayan zaben fidda gwani na gwamna na jam'iyyar PDP a watan Mayun 2022 wanda ya samar da Dauda Lawal a matsayin wanda ya yi nasara.

A lokacin ne gwamnan ya lura da kuskuren da ya yi na rashin kara Dauda a cikin jerin wanda zai ‘tare masa hanya’. An yi ta rade-radin cewa Gwamna Matawalle ne ya dauki nauyin wani fusataccen dan takarar gwamna, Shehu Bakauye, domin ya nuna rashin amincewa da yadda jam’iyyar PDP ta gudanar da zaben fidda gwani.

Kasancewar Dauda a fafatawar, Gwamna Matawalle ya yi hasashen za a samu koma baya a sake zabensa, duk da cewa Yari da Marafa suna ta tausasa shi da fata na karya.

Duk da haka, zuciyar Matawalle ta ci gaba da ingiza shi da ya yi amfani da kotu domin dakile damar Dauda. Mun shaida yadda wani Alkalin wata babbar kotun tarayya da ke Gusau ya yi rawa ga kidar da gwamnan ya yi, inda a lokuta daban-daban guda biyu ya soke zaben fidda gwanin da ya samar da Dauda Lawal.

Kotun daukaka kara da ke zamanta a Sakkwato, a hukuncin da ta yanke, ta mayar da Dauda Lawal a matsayin wanda ya yi nasara. Hukuncin da ya karawa Dauda kuzari ya kuma kasance koma baya ga Matawalle da APC.

A cikin kasa da wata guda, sunan Dauda Lawal ya zama abin ambato a gidaje a kauyuka da garuruwa a fadin jihar. Shahararriyar motar kamfen din ‘Bazamfara’ ta yi barna sosai a yunkurin Matawalle na sake ganin an zabe shi a takararsa ta biyu fiye da kokarin da Yari da Marafa suka yi wajen ganin ya samu nasara.

Lawal ya ji daɗin tumbatsar farin jininsa a ranar. Salonsa, dagewarsa, da sahihancinsa na siyasa ya ba shi babban kima. A karon farko a tarihin jihar, dan takarar gwamna ya kaddamar da yakin neman zabensa tare da kaddamar da manufofinsa.

Manufofin Lawal mai dauke da nagartattun kudurori shida ya sanyawa mutane fatan cewa wani sabon mai jini a jika ya shiga fafatawar domin ceto. Taken yakin neman zabensa, ‘Ceto da Gina Zamfara,’ ya fallasa gaskiyar jihar.

Dauda ya yi yakin neman zabe a daukacin kananan hukumomin jihar 14 ba tare da tara ‘yan daba ko jama’ar haya ba. A kafatanin lokacin yakin neman zabe, Lawal ya nuna matukar kamun kai da rashin son ‘yan bangar siyasa. Ya kan roki ‘yan sanda da su kare allunan talla da tutocin ‘yan adawa daga taron masu zumudi. Na shaida hakan a wurare da yawa.

A takaice dai, ina bayyanawa jama’a cewa dukkanin wadanda ake kira da ‘jiga-jigai’ a Zamfara; ko ya kasance Yari ne ko Yarima; Marafa ko Matawalle; Shinkafi ko Jaji duk sun yaki Dauda da dukkan karfinsu, amma ba su yi nasara ba. Kada a yaudare ku!

Bala ya rubuto ne daga Gusau kuma za a iya samunsa ta isbdaurawa@gmail.com

Fassarar Muhammad A. Abubakar

No comments