Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Pages

Labarai:

latest

Zargin Batanci Ga Annabi (S): Yadda Izala Da Malaman Salafiyya Suka Shiga Suka Fita Aka Dakatar Da Tittsiye Sheikh (Dakta) Abdul'aziz Dutsen Tanshi

*Almajiransa sun yi barazanar tarwatsa zaman lafiyar Nijeriya *Yadda kare martabar Manzon Allah (S) ke neman juyewa zuwa fadan akida Dag...

*Almajiransa sun yi barazanar tarwatsa zaman lafiyar Nijeriya

*Yadda kare martabar Manzon Allah (S) ke neman juyewa zuwa fadan akida

Daga Muhammad Farouk

Ana ci gaba da mayar da kausasan martani a tsakanin Malaman addinin Musulunci a cikin watan Ramadan dangane da zargin da ake yi wa wani Malami dan kungiyar Salafiyya dake garin Bauchi, Sheikh Abdul’aziz Idris Dutsen Tanshi.

Zargin ya samo ne dangane da wata kalma da Shehin Malamin ya gayawa Manzon Allah a yayin da yake mayar da martani ga wata waka da aka yi wa Manzon Allah (S). Lamarin dai ya jawo cece kuce a tsakanin al’ummar Musulmi wanda ta kai ga Malamai da dalibai da sauran gama garin al’umma ke ta kira ga gwamnatin jihar Bauchi da ta kama Malamin tare da yi masa tittsiye.

Sai dai da dukkanin alamu lamarin kare martabar ta Manzon Allah (S) ya juye ya koma fadan akida, a inda bangaren Izala/Salafiyya suke kallon lamarin a matsayin bangaren Darikun Sufaye da Shi’a na yakar akidarsu ne lamarin da dukkanin bangarorin suka musanta.

Bayanai da rahotanni da suka bayyana a shafukan sada zumunta sun nuna yadda wasu Malamai bangaren Izala da Salafiyya suka barranta wadannan kalamai na Dr Abdul’aziz Idris Dutsen Tanshi. A yayin da mafi yawan Malaman Izala da Salafiyya fitattu a Arewacin Nijeriya suka nuna goyon bayansu ga da’awar ta Dr Abdul’aziz Idris Dutsen Tanshi lamarin da ya sake fusata al’ummar Musulmi.

A ranar 6 ga watan Afrilun 2023, Gwamnatin jihar Bauchi ta gayyaci Dr. Idris  Dutsen Tanshi domin zuwa ya kare kansa bisa zargin 6atanci' ga Annabi Muhammadu (SAW).

Sanarwar ta fito ne a wata takarda daga Hukumar shari'a ta jihar Bauchi wanda Shugaban hukumar, Ibrahim Musa Yisin ya sanyawa hannu kuma Jaridar MADOGARA ta samu kwafinta.

Takardar ta fara da cewa; “Bisa umurni ina rubuto maka gayyata a hukumance zuwa ga wata tattaunawa (munakasha) domin karin bayani kan wasu kalamai da ka yi a lokacin Tafsirin Ramadan idan ka ce; "Kai! Na Manzon Allahn ma ba mu son taimakonsa karewarta ke nan".

Takardar ta ci gaba da cewa; “Gamsasshen karin bayaninka zai taimaka wajen rage tashin hankalin da al'ummar Musulmi ta fada (sakamakon kalamanka), tare da samar da dawwamammen zaman lafiya a tsakanin al'ummar Musulmi".

Ibrahim Musa Yisin ya tabbatar da cewa za a gudanar da zaman wannan tattaunawar ne a ranar Asabar 8 ga watan Afrilun 2023 da misalin karfe 10 na safe a DEC (Development Exchange Centre) dake titin Ahmadu Bello Way dake Bauchi.

A karshe hukumar ta shawarci Malamin da ya daure ya halarci zaman.

Aikawa da wannan takarda ke da wuya, Dr Abdul’aziz Dutsen Tanshi a yayin gabatar da Tafsirin Ramadan cikin kwarin guiwa ya ce a shirye yake ya halarci wannan zaman tattaunawar domin “ni kadai gayya”, inji shi a wani faifan bidiyo da shafin da ake yada karatuttukansa suka wallafa.

Sai dai fitar wannan sako ke da wuya a washegari, kungiyar Jama’atu Izalatul Bidi’a wa’ikamatus Sunnah (JIBWIS) reshen jihar Bauchi ta ce ta janye halartar zaman da za a yi da Dr. Idris Dutsen Tanshi, tana mai cewa; kamata ya yi a yi wa Malamin nasiha idan ana ganin ya yi amfani da wasu lafuzan da bai kamata ba. Domin a cewar JIBWIS zantukan Malamin kan Manzon Allah (S) batu ne da ya shafi akidarsu.

Iliyasu Danjuma Bandas, Sakataren JIBWIS na Bauchi shi ne ya tabbatar da hakan a takardar da ya aikewa da Hukumar Shari’a ta Bauchi kan batun janyewarsu daga halartar zaman tattaunawar mai dauke da kwanan wata 7 ga watan Afrilun 2023.

“Da fatan za ka fahimce mu, kuma Allah ya yi mana kyakkyawan jagora, Amin”, a cewar bayanin takardar.

A wannan ranar an ga ganga-gangar gamayyar taron Malaman Izala/Salafiyya daga garuruwa daban-daban da ya hada da Kano, Zamfara Kaduna da sauran su suka dira a garin Bauchi a inda Malamin yake gabatar da jawabi domin ba shi kariya.

Jaridar MADOGARA ta labarto cewa; almajiran Sheikh Dr Idris Abdul’aziz Dutsen Tanshi dake garin Bauchi, sun bayyana cewa su a shirye suke su mutu da wani abu ya taba farcen Malaminsu. Malam Abdallah wanda ya zo daga Kano shi ne wanda ya bayyana hakan a madadin almajiran Shehin Malamin a daren ranar Juma’a a Masallacin Malamin dake Bauchi.

A yayin da Malam Abdallah ke wannan bayanin, almajiran Shehin Malamin dake cikin Masallacin sun rika kwantsama kabbara suna mai jaddada abin da Malam Abdallah ya fadi a yayin da Dr Idris Abdul’aziz Dutsen Tanshi ke gefe yana saurarensu.

Malam Abdallah ya ci gaba da cewa; “duk wanda ya ci mutuncin Malam, na rantse da Allah rigimar addini ce za ta barke wacce babu ranar da za a toshe ta”, nan take mahalarta a masallacin suka barke da kabbara mai karfi.

“Ba wani dan sanda da ya kira, Ubangiji ne kawai ya sanya min a raina cewa mutanen nan wulakantaka suke son su yi. So suke su tozartaka”, inji Malam Abdallah a gaban Dr Idris Dutsen Tanshi.

A don haka Malam Abdallah ya tabbatar da cewa Malaminsu Dr Idris Dutsen Tanshi ba zai halarci zaman tattaunawar da hukumar shari'a ta jihar Bauchi ta shirya ba. Ya kuma tabbatar da cewa fahimtar Malamin na su ita ce akidarsu.

Dr Idris Dutsen Tanshi har wala yau a jawabinsa a wannan dare a gaban almajiran na shi ya yi zargin cewa ana shirin kai shi gidan yari da rusa masa masallacinsa, inda ya ce; “ya ce wallahi Malam abin da ake nufi da maganar mukabala din nan; bayan mukabala ana son a kama ka. Bayan an kama ka za a kai ka kotu, ana kai ka kotu, Alkalin zai tura ka gidan gyaran hali, idan ya tura ka gidan gyaran hali daga baya masallacinka za a rusa shi”, inji shi a lokacin da yake labarta abin da wani ya gaya mishi.

Wadannan kalamai na tunzuri ya sanya a wata sabuwar sanarwa da Hukumar Shari’a ta Bauchi ta fitar, wanda shugabanta Ibrahim Musa Yisin ya sanyawa hannu ya ce sun dage zaman tattaunawar na ranar Asabar 8 ga watan Afrilu, za su sanar da sabuwar ranar da za su yi zaman tattaunawar.

“ina mai sanar da kai a hukumance cewa an sauya ranar gabatar da wannan tattaunawar kamar yadda aka tsara a ranar 8 ga watan Afrilun 2023.

“Za mu sanar da kai sabuwar ranar da za a sanya yadda ya dace”, sanarwar ta tabbatar.

Hukumar shari’a ta yanke wannan hukunci ne bayan tabbatar da cewa gamayyar Malamai da almajirai masu goyon bayan Dr Idris Dutsen Tanshi daga bangaren Izala da Salafiyya sun dira a masallacin Malamin domin ba shi kariya tare da jaddada goyon bayansu ga kalaman Malamin tare da shelanta kalaman tashin hankali.

Har wala yau a wata takarda da hukumar shari’a ta Bauchi ta fitar mai dauke da kwanan wata 12 ga watan Afrilun 2023, ta bayyana cewa ta karbi dukkanin korafe-korafe daga bangarori daban-daban za ta sanar da sabon matakin da za ta dauka wanda zai wanzar da zaman lafiya a fadin jihar.

Har wala yau Kwamishinan Shariah na jihar Bauchi mai suna Malam Mustapha Baba Ilela, ya yi bayanin yadda lamarin ya kasance tunda fari da kuma yadda a karshe Æ´an'uwan Dr Abdul’aziz Dutsen Tanshi a akida wato bangaren Izala da Salafiya suka canzawa lamarin wata fuska ta daban ya koma kamar fadar kungiyanci.

Wannan lamari ya soma aukuwa ne a yayin da Dr Idris Dutsen Tanshi yake mayar da martani kan wani waken yabo na fiyayyen halitta da wasu ‘yan wasan Hausa suka yi wanda aka fi saninsu da ‘yan Kannywood, Shehin Malamin ya ce; "Kai! Na Manzon Allahn ma ba mu son taimakonsa karewarta ke nan".

Yanzu dai ya zuwa hada wannan rahoton, bangaren Izala/Salafiyya suna kallon lamarin a matsayin yaki da akidarsu ba wai kare martabar Manzon Allah (S) ba, a yayin da bangaren sauran al’ummar Musulmi ke kallon abin a matsayin dole a tashi a yaki masu taba janibin Manzon Allah (S) da sunan Tauhidi ta hanyar gaya wa Manzon Allah (S) magana, izgili ko gatse. 

No comments