Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

Alummar Turkiya na gudanar zaben da zai fayyace makomar Erdogan

A yau Lahadi Turkiyya ke gudanar da zaben da ka iya tsawaita wa’adin mulkin shugaba, Recep Tayyip Erdogan, wanda ya shafe shekaru 20 yana ja...


A yau Lahadi Turkiyya ke gudanar da zaben da ka iya tsawaita wa’adin mulkin shugaba, Recep Tayyip Erdogan, wanda ya shafe shekaru 20 yana jagorancin kasar.

Zaben shugaban  kasar da na ‘yan majalisar dokoki ya rikide zuwa wat kuri’ar jin ra’ayin al’umma a kan shugaban Turkiyya mafi dadewa  kan karagar mulki da jam’iyyarsa, kuma shine mafi sarkakiya daga  cikin zabukan da shugaba Erdogan ya taba fuskanta, inda wasu ke gaanin yana iya faduwa.

Erdogan mai shekaru 69, ya jagoranci kasar  mai yawan al’umma miliyan 85 zuwa ci gaba da aka dade ba gani ba a cikin shekaru 100 na bayan daular Usmaniyya.

Irin tasirin da Turkiyya ta yi a harkokin da suka shafi Turai da Gabaas ta Tsakiya a ‘yan shekarun baya bayan nan  matsayin na daya daga cikin mambobin kungiyar tsaro ta NATO ya sa wannan zabe ya kasance da mahimmaci ga Amurka da Tarayyar Turai, kamar yadda yake ga Turkiyar kanta da Rasha.

No comments